Masu zuwa daurin aure 20 sun rasu bayan motarsu fada kogi a Kenya
Masu aikin ceto na ci gaba da aiki bayan nutsewar motar a cikin kogi
Akalla mutum 20 sun rasu a hanyarsu da zuwa wani bikin daurin aure bayan motarsu ta fada a cikin kogi a kasar Kenya.
Masu zuwa daurin auren sun rasu ne bayan motar da ke dauke da su ta kwace a kan wani gada ta fada a cikin kogin a ranar Asabar.
- Minista ya sauka daga mukaminsa kan mutuwar mai sharar titi
- Masu ibada 60 da aka yi garkuwa da su a Kaduna sun kubuta
“Masu aikin ceto na kokarin ganowa da ceto su, amma zuwa yanzu an gano gawarwaki 20,” inji Kwamandan ’Yan Sandan yankin Mwingi ta Gabas, Joseph Yakan.
Karin bayani na tafe.