Mata sun yi zanga-zanga don bacewar ‘ya’yansu a Borno
Wasu iyaye mata sun yi zanga-zanga a yau Alhamis don bacewar ‘ya’yansu da sanin inda suke. A cewar su ‘ya’yan sun bace ne bayan da jami’an tsaro suka kama su akan alakar su da ‘yan Boko Haram kimankin shekara shida kenan.