Mata ta dabawa mijinta wuka ya mutu a Kebbi
Wata matar aure mai suna Hafsat Sani ta dabawa mijinta mai suna Muhammed Garba wuka ya mutu a karamar hukumar Suru jihar Kebbi. Hafsat mai shekara 25 ta kashe mijinta ne bayan wata gardama da suka yi a gida su da ke kauyen Tundifari a karamar hukumar Suru, Hafsat ta dabawa Muhammed wuka ne a […]
Wata matar aure mai suna Hafsat Sani ta dabawa mijinta mai suna Muhammed Garba wuka ya mutu a karamar hukumar Suru jihar Kebbi.
Hafsat mai shekara 25 ta kashe mijinta ne bayan wata gardama da suka yi a gida su da ke kauyen Tundifari a karamar hukumar Suru, Hafsat ta dabawa Muhammed wuka ne a ciki.
Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kebbi, Mista Garba Mohammad Danjuma, ya tabbatarwa manema labarai cewa, a yanzu haka sun kama Hafsat yayin da ake ci gaba da biciken dalilin kisan mijinta.