Matar mataimakin Gwamnan Neja ta rasu
Allah Ya yi wa Hajiya Zainab, matar Mataimakin Gwamnan Jihar Neja, Yakubu Garba rasuwa.
![Matar mataimakin Gwamnan Neja ta rasu Matar mataimakin Gwamnan Neja ta rasu](https://aminiya.ng/wp-content/uploads/2024/07/IMG-20240702-WA0021.jpg)
Allah Ya yi wa Hajiya Zainab, matar Mataimakin Gwamnan Jihar Neja, Yakubu Garba rasuwa.
Hajiya Zainab ta rasu ne a asibiti bayan gajeruwar rashin lafiya.
Mutuwa ta riske ta ne a wani asibiti da ke Minna, babban birnin jihar a ranar Talata.
Gwamnan jihar, Mohammed Umaru Bago, ya bayyana alhini da game da wannan rashi.
Sakon ta’aziyyar da kakakinsa, Bologi Ibrahim, ya sa wa hannu ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ga jihar.
Ya kuma yi addu’a Allah Ya sada ta da mafificin rahama a Aljanna Firdausi, Ya ba wa mijinta hakurin jure wannan rashi.