Matar mataimakin Gwamnan Neja ta rasu

Allah Ya yi wa Hajiya Zainab, matar Mataimakin Gwamnan Jihar Neja, Yakubu Garba rasuwa.

Matar mataimakin Gwamnan Neja ta rasu

Allah Ya yi wa Hajiya Zainab, matar Mataimakin Gwamnan Jihar Neja, Yakubu Garba rasuwa.

Hajiya Zainab ta rasu ne a asibiti  bayan gajeruwar rashin lafiya.

Mutuwa ta riske ta ne a wani asibiti da ke Minna, babban birnin jihar a ranar Talata.

Gwamnan jihar, Mohammed Umaru Bago, ya bayyana alhini da game da wannan rashi.

Sakon ta’aziyyar da kakakinsa, Bologi Ibrahim, ya sa wa hannu ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ga jihar.

Ya kuma yi addu’a Allah Ya sada ta da mafificin rahama a Aljanna Firdausi, Ya ba wa mijinta hakurin jure wannan rashi.