Matsalar tsaro: Buhari ba zai yi murabus ba- Gwamanatin Tarayya
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ba zai yi murabus daga mukaminsa ba, saboda kalubalen tsaron kasar. Ministan yada labarai da al’adun Najeriya Lai Muhammed, ne sanar da hakan ranar Alhamis yayin da yake tattaunawa da manema labarai. Ministan ya mayar da martanin ne game da yadda wasu ke yin kira ga Shugaban ya yi murabus saboda […]
Shugaba Buhari
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ba zai yi murabus daga mukaminsa ba, saboda kalubalen tsaron kasar.
Ministan yada labarai da al’adun Najeriya Lai Muhammed, ne sanar da hakan ranar Alhamis yayin da yake tattaunawa da manema labarai.
Ministan ya mayar da martanin ne game da yadda wasu ke yin kira ga Shugaban ya yi murabus saboda tabarbarewar tsaro a kasar. “Shugaban kasar ba zai yi murabus ba, har sai ya cika alkawarin da ya yi wa ‘yan Najeriya na yi masu aiki zuwa karshen wa’adin mulkinsa zuwa watan Mayu na shekarar 2023.” In ji Ministan.