Matsalar tsaro: Buhari zai bayyana gaban majalisa

Shugaban zai yi wa majalisar bayani kan matsalar tsaro.

Matsalar tsaro: Buhari zai bayyana gaban majalisa

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari

Kakakin Majalisar Wakilai, Femi Gbajabiamila ya ce Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya amince ya bayyana gaban majalisar don yi wa ‘yan Najeriya bayani game da matsalar tsaro.

Gbajabiamila ya bayyana hakan ne ga ‘yan jarida a ranar Laraba, jim kadan bayan ganawa da shugaba Buhari a fadar Villa dake Abuja.

Kakakin ya ce Buhari zai bayyana gaban majalisar ne domin yi wa ‘yan Najeriya cikakken bayani game da matsalar tsaro da take kara tabarbarewa a kullum.

Sai dai bai bayyana ranar da Buhari zai bayyana gaban majalisar ba, inda yace sai nan gaba kadan za a sanar da ranar ga ‘yan kasa.

Ya kara da cewa ‘yan majalisar sun koka game da halin da kasar ke ciki, wanda hakan ne yasa ya amince ya bayyana gaban majalisar domin yi mata bayani.

Kakakin majalisar ya ce Buhari shugaba ne dake martaba dimokuradiyya saboda amincewarsa da gayyatar.

Gbajabiamila ya ce Buhari ya damu matuka da halin da kasar nan ke ciki na matsalar tsaro.

Sojoji sun kashe kwamandan ’yan bindiga da tarwatsa 300

Zaɓen 2027: Tinubu ya sake tsayar da Shettima mataimakinsa

Tinubu ya gaji yana buƙatar ya huta — Peter Obi

Ɗalibai da malamai da aka sace a Oyo sun kuɓuta