Matsalar tsaro: Samar da ’yan sandan jihohi ne mafita – Gwamnan Neja

Kwanan baya  Gwamnan jihar Neja Alhaji  Abubakar   Sani Bello  ya kai ziyara  Amurka kuma  ya tattauna  da  wakilinmu  a birnin Washinton DC kan batutuwa  daban-daban. Ga yadda hirar ta kasance: Aminiya: Ta  yaya  wannan taron da kuka yi zai  shafi  mutanen jihar Neja?Lallai  mun tattauna kan batutuwa  da  dama, wanda  kuma  tsaro  shi ne kan […]

Matsalar tsaro: Samar da ’yan sandan jihohi ne mafita – Gwamnan Neja

Kwanan baya  Gwamnan jihar Neja Alhaji  Abubakar   Sani Bello  ya kai ziyara  Amurka kuma  ya tattauna  da  wakilinmu  a birnin Washinton DC kan batutuwa  daban-daban. Ga yadda hirar ta kasance:

Aminiya: Ta  yaya  wannan taron da kuka yi zai  shafi  mutanen jihar Neja?
Lallai  mun tattauna kan batutuwa  da  dama, wanda  kuma  tsaro  shi ne kan gaba, kuma an fi  magana  ne  a kan mutanen jihar Borno,  inda nan ne ake samun rikicin ‘yan Boko  Haram, da kuma  mutanen da suka yi  hijira  daga  gidajensu suka koma sansanin ‘yan gudun hijira, wadanda kuma  gwamnan jihar Borno  ya yi  bayanin halin da suke  ciki, musamman na  irin halin yunwar  da  mutane ke fuskanta  a  wadannan sansanonin da  kuma  irin taimakon da  suke  bukata.
Kuma  an yi  maganar  tsaro  da ya  shafi  arewacin Najeriya gaba  daya, misali,  ni  bayanin  da na yi  a kan  barayin da ke  satar mutane da  masu  satar  shanu ne. A gaskiya  mun tattauna  sosai  game da  tsaro,  domin duk  al’ummar  da  ba ta  da tsaro to  babu  yadda za a yi  abubuwa su  tafi daidai. Kuma kowane  gwamna ya  samu  dama  ya yi  bayanin  irin hali  tsaron da  jihar take ciki.
Aminiya: Wane irin taimako ne gwamnatin Amurka za ta  ba ku?
Mun zauna da  sakataren harkoki wajen Amurka John Kerry da  kuma  Susan Rice. Shi  Kerry  bayan mun gama tattaunawa  da shi  ya bukace  mu  da mu  mika  bukatunmu a rubuce na iri taimakon da muke  so  su yi  muna.
Aminiya: A jihar Neja  me kake yi  domin inganta kudin shiga, kuma  me gwamnatinka tayi  daga  lokacin da ka karbi  ragamar  mulki  kawo  yanzun?
Allah Ya sa mun shigo a lokaci da  babu  kudi, gaskiya a jihar Neja  ban  tsammanin an taba  kaiwa  lokacin da  har albashi  yana  gagara  ba,  sai  wannan  karon, domin a wasu kwanakin da suka gabata  mun samu matsalar  biyan albashi,  amma Allah cikin ikonSa Ya sa  aka warware. Amma  na tabbata har ga Allah duk  mai  nema yana tare  da  samu  kuma  muna iyakar kokarinmu, domin komi a jihar ya  dan dakata, abubuwa da  yawa  sun lalace,  makarantun sun lalace, daga firamare har zuwa sakandare, inda za ka ga  yara  na daukar  karatu  a kasa  ko  kuma suna kwance a kasa  ko  wurin cin abinci  kamar na  dabbobi. Wannan ya sa  muka  bai wa  ilmi  muhimmaci  a  cikin abin da  muke  fata mu yi,  don haka yanzu  mun fara  gyaran makarantu, musammam makarantun kwana. Ina fata  lokacin da  za a  kammala  aikin gyaran wadannan makarantun  to  duk wanda ya kai  ‘ya’yan sa  makarantar  kudi  sai  ya  fidda  su  ya  dawo  da su  na  gwamnati.
Aminiya: Kana ganin za ka iya gyara  daukacin makarantun kwana da ke cikin jihar  har su zama  abin alfahari?
Sai dai  inyi bakin kokarina, fata  shi ne  wanda zai  karba  daga  gare ni  ya  dora,  domin abin da  yawa. matsalolin da ke kasa na makarantu da sauran abubuwa  Allah Ya yi  yawa  da su.
Aminiya: Za ku karbi wani ne daga iyayen  yara  domin tallafa wa  fannin ilmi?
Yanzu  haka  dai  na kafa kwamitin da  zai  samar  muna  yadda  za a samu  kudin shiga  kuma  ba  zan sanya musu  baki  ba, zan barsu suyi aikinsu, amma batun sanya  haraji  ga  iyayen yara zai yi  wuya, domin ko  a nan Amurka da muka  tattauna  mun yi  maganar  ilmin ‘ya’ya mata, yayin da muke son mata  su je makaranta  idan muka bullo da batun haraji a makaranta  gaskiya  zai yi wahala.
Aminiya: Ko da  kamar  Naira  goma  ko ashirin?
Ai Naira goma  ko  ashirin a  halin rashin abincin nan kudin kamar  Naira miliyan ne  a  wurin wani, domin wani  idan ka ba shi  Naira goma ko  ashirin ko  hamsin, kila  ma  tunda  safe   bai  ganta ba,  kuma  ka ce  irin wannan mutumin ya  kawo  ta a matsayin haraji, kai  ka san aiki  ne babba.
Aminiya: Me kake yi  game  da gyaran hanyoyi,  duk  da  yake wadansu a karkashin gwamnatin tarayya suke?
Kwanaki  na  gyara  hanya  daga  Minna har  zuwa  Suleja, amma yau idan ka  biyo  hanyar  nan sai  ka ga kamar  ba a  taba gyaranta  ba. Saboda hanya tsakanin Makera  Tegina zuwa Birnin Gwari  har Kaduna akwai  gadojin da  wurare  da  yawa  da suka lalace, manyan motoci  sun daina bi, kusan gaba dayansu  sun koma  bi ta Bida su wuce  Legas, ba  yawan motocin ne matsala ba, amma  irin kayan da  suke dauka ne  abin  damuwa domin ya yi  yawa. Abin da  muka  sani  shi ne,  mota  tirela ba ta  wuce  ton 30 zuwa 36,  amma yau suna  daukar  ton 36 ko 40, kai  wadansu  har 60 zuwa 70   suna  dauka, dole hanya  ta fashe. Na ga inda  tirela ke tafiya hanya  yana  fashewa saboda nauyi,  wannan nine  na gani  ba wai wani ne ya fada mani  ba. Kuma  hanyoyinmu  na Najeriya  ana yinsu  domin ton dubu 30  zuwa  35. A da  akwai  wadansu  wurare  da ake auna  nauyin tirela, idan ta zo dole ne ta  hau  a ga  nauyi kayan da ta  dauka,  amma a yau  duk  babu wadannan, duk inda  gwamnbati ta  kashe  kudi  wajen gyaran hanya  na  kwana biyu ne  kawai. Yanzu  wannan hanyar  da na  gyara  kamar ba a taba  gyaranta  ba.
Kwanakin baya  na yi  magana da shugaban kasa  cewa  a taimaka, misali  hanyar da tashi daga  Kamfanin Bobi zuwa Kasuwar Garba  zuwa Bangi zuwa Gulbin Boka, akwai  kuma  hanya  daga Gulu zuwa  Ebute  zuwa Lambata, akwai kuma  hanya  daga  Pandogari  zuwa Alawa Erina zuwa Shiroro, sannan akwai  daga Lumma zuwa  Agwara  zuwa Rofiya. Kuma  ya tabbatar  mani  gwamnati tarayya za ta taimaka, ina  ganin babu wata  jihar da take  da  yawan hanyoyi na gwamnati tarayya  kamarmu, shi  ya sa  muke shan wahala.
Zan gabatar  da maganar gaban gwamnoni. Ba za mu  hana  kasuwanci  ba, amma  kamata  ya yi  tirela ta  dauki  kaya  daidai  da  abin da  titi  zai iya  dauka, wato  ton dubu 33 zuwa  da  36,  shi ne  wanda muka saba da shi, muddin mun  tsare, wannan hanya  zai yi kyau, za  a  samu raguwar  lalacewar  hanyoyi, amma  idan ba haka ba  ana  gyara  hanyar ne tana kara  lalacewa.  Kuma wa ke  shan  wahala, mu  mutanen kasa  muke shan wahala,  saboda  yawancin masu  kamfanonin tirelolin ba su  tafiya  kan hanya  sosai balle  su ga  irin abin da  motocinsu ke  haifarwa. Domin kullum ana  hadari  motoci  na  faduwa, mutane  na mutuwa, wannan yana  iya  shafar ko ma wane ne.
Akwai wani  direban tirela  da na tambaye shi me  ya sa  suke daukar  kayar  da  ya  wuce  ka’ida, sai ya ce shi har  ton dubu 60 yana  dauka,  kuma  shi da  mai  daukar  ton dubu 30  albashinsu  daya  ne.
Aminiya: Wadansu jihohi  na so a  ba su  damar  samar da ’yan sandar jiha, kana  jin  cewa hakan zai taimaka wa  harkokin tsaro?
kwarai  zai taimaka, saboda  yanzu  idan ka  duba  wurare  da  yawa ’yan banga  ne  suke  taimaka wa  harkokin tsaro, ka ga  a da  ta bangaren  satar  mutane a kan kawo  mana  gudunmowar bayanan sirri, amma yanzu sun bari. Domin idan suka kawo  aka tafi aka  kama  mutum,  bayan kwana  biyu  sai ka  tarar  an saki  mutumin, shi  kuma  sai ya nemi  wanda  ya ba da  wannan bayanin, wata  sa’ilin ma  har  a  kashe  shi.
Aminiya:  ‘Yan sandan gwamnatin  tarayya  ke nan sukan  yi  haka,  ina  ga  a ce  ‘yan sandan  gwamnatin jiha ne?
Da  ‘yan sandan gwamnatin tarayya  da na  jihohi  duk  daya ne, za ka  ce  mene ne hujja, abin da  za a ce shi ne idan jihohi  suka  samu  ‘yan sanda  za a ce  gwamna  zai yi  duk  abin da  ya ga dama, to  su ma  na  gwamnatin tarayya  idan shugaban kasa ya ga  dama  zai yi  abin da  ya ga dama da ’yan sanda .
Aminiya: Yanzu  ma  da suke  ba  karkashin gwamnatocin jiha suke ba idan ta kai ta dawo Gwamna na iya  yin yadda  ya ga dama  da su, me  za ka ce?
Idan  ba ka  kai ka  kawo  ba kuma  fa?
Aminiya: Akwai mutumin da  ya kai  mukamin gwamna a Najeriya kuma  bai kai  ya  kawo  ba?
kwarai kuwa, kuma ni  gwamna  ne  nake fada  maka  haka,  akwai  gwamnonin da kafin su  samu  wani  abu  sai  sun yi kamun kafa  ko  kuma  lallabawa  ta  wurin wadansu  takwarorinsu  gwanoni.
Aminiya: Gwamnatin tarayya  ta  gabatar da  shirin a  koma  noma, shin ina  matsayin jihar Neja a  cikin  wannan shirin?
Gaskiya mun gode  wa  gwamnatin Janar Muhammudu  Buhari  ta bangaren noma, da  kuma  gwamnan babban bankin Najeriya,  domin sun bullo  da  wani shiri da  ake kira da turanci Anchor Borower Scheme, wanda kuma  gwamnatin jihar Kebbi  ta  fara kuma  gwamnonin jihohin  Arewa  wasu  ma  suna  yi, inda  ake taimaka wa  manoma, a yi musu rajista, kamar  mu  jihar Neja  mun yi sa’a,  domin kamar  a wasu  jihohi  shinkafa  kawai  ake  yi, amma  mu  a namu  shirin za a yi  shinkafa a yi  auduga, kana  a yi  waken soya, kuma  ni  na tabbata  a Najeriya nan da  shekara  daya zuwa  biyu idan  dai maganar abinci   ne  za a  samu  sauki, domin  wannan shekarar an noma  shinkafa  sosai,  mutane sunyi  noma, sai dai mu  a  jihar Neja  ta  wani  bangare  an samu  ambaliya, wannan ya sa an dan samu  asarar shinkafa sosai, amma  duk  da  haka  za a samu  abin da aka samu.  Kuma halin da  ake ciki a Najeriya kowa  ya sani, wanda  wannan ya sa  mutane da  yawa  sun koma  harkar noma, kuma gaskiya na ji  dadin haka, domin tun farko  shi ne  muka gada,  domi ba mu  da mai, amma  idan muka  rike  noma, to  lallai  arzikin arewacin Najeriya  zai  karu  sosai.
Aminiya: Ko kana  tunanin duba  kamfanin sarrafa shinkafa na Badegi?
Badegi na nan an samu wani  kamfani da zai  ci  gaba  da  aiki  a  wurin, tun lokacin da  waccan gwamnatin ta wuce aka  samu  ‘yan matsaloli, amma  yanzu  ina  ganin an dan warware, kuma yanzu  haka muna  magana da kamfanin, ina  ganin kwanan   zai  bude  a fara  aiki.
Aminiya: Kana  tunanin shiga  wata yarjejeniya  a kan gonar  Mokwa, duk  da yake  gonar mallakar  gwamnatin tarayya  ce?
kwarai kuwa, ai kaga a Asiwashi  akwai ’yan indiya  masu  nomar shinkafa, akwai  wata  gona  a wajen Kidi gwamnatin ta fara  ta bari, muna  kokarin ganawa  da su  domin mu ga  yadda  za mu amfana  da shi, akwai   abubuwa  da  yawa  wadanda zasu  taimaka wa noma wanda ina son ganawa da ministan gona  domin ganin yadda za mu hada  kai saboda  amfanin jama’ar jiharmu  da ma kasa  baki daya.Kuma  akwai manoma  da  yawa  da  suka fara  girbi  muna  son mu ga  yaya  za a  taimake su domin a  sayi hatsin nan daga  gare  su  domin su  samu  kudi.
Aminiya: Wadansu na zargin gwamnatika  ta ki  ta  binciki  wadda  ta gada, me  za ka  ce?
Wannan ba  gaskiya ba ne, ana  bincike, domin mun kafa  kwamiti  kuma  an kira  dukkan kwamishinonin da suka sauka domin su yi bayani, bincike  ana yi, mutane  su yi  hakuri, su bi a hankali,  ni kaina  na matsu  a  samo  wani  abu  daga  wurinsu domin mu kara  cikin aikinmu, kuma akwai  wadanda  aka  samu  wurin wadanda suka ci  kudin ‘yan fansho,  an karbo  wani  abu  daga  hannunsu, amma wannan baitulmalin ‘yan fansho  za  a  mayar da  kudaden.