Mayakan Boko Haram sun kaddamar da hari a Damboa
Mazauna garin dai na zargin mayakan sun lalata turakun sadarwa.
Mayakan Boko Haram
Rahotanni daga garin Damboa na Jihar Borno sun ce yanzu haka mayakan kungiyar Boko Haram na can sun kaddamar da hari a Karamar Hukumar.
Wata majiya daga jami’an tsaro ta shaida wa Aminiya cewa ’yan ta’addan sun shiga garin ne da misalin karfe 5:00 na yammacin Asabar.
- Dalilin da har yanzu nake jinyar tiyata a Landan – Tinubu
- Babu kasar da ta ci gaba ta amfani da harshen aro – Masani
A cewar majiyar, jim kadan da kai mamayar mayakan a garin, hanyoyin sadarwa sun dauke, lamarin da ya sa ake zargin sun lalata turakun sadarwar garin.
Yanzu haka dai dakarun sojoji na can suna fafatawa da ’yan kungiyar ta Boko Haram.