Mayakan Boko Haram sun kaddamar da hari a Damboa

Mazauna garin dai na zargin mayakan sun lalata turakun sadarwa.

Mayakan Boko Haram sun kaddamar da hari a Damboa

Mayakan Boko Haram

Rahotanni daga garin Damboa na Jihar Borno sun ce yanzu haka mayakan kungiyar Boko Haram na can sun kaddamar da hari a Karamar Hukumar.

Wata majiya daga jami’an tsaro ta shaida wa Aminiya cewa ’yan ta’addan sun shiga garin ne da misalin karfe 5:00 na yammacin Asabar.

A cewar majiyar, jim kadan da kai mamayar mayakan a garin, hanyoyin sadarwa sun dauke, lamarin da ya sa ake zargin sun lalata turakun sadarwar garin.

Yanzu haka dai dakarun sojoji na can suna fafatawa da ’yan kungiyar ta Boko Haram.