Ministan Birtaniya ya yi Sallah a Masallaci Kudus

Minista Tariq Ahmad ya jaddada goyon bayan Birtaniya kan barin ikon wurare masu alfarma a birnin Kudus a karkasin ikon kasar Jordan.

Ministan Birtaniya ya yi Sallah a Masallaci Kudus

Ministan Birtaniya kan Yankin Gabas ta Tsakiya da Arewacin Afirka da Kudancin Asiya da Majalisar Dinkin Duniya a Ofishin Kula da Kasashe Rainoin Ingilata, Tariq Ahmad, ya yi Sallah a Masallacin Kudus a ziyarar da ya kai ranar Alhamis.

Bayan nuna farin cikinsa bayan ya idar da Sallah a Masallacin da ke Gabashin Birnin Kudus, Minista Tariq Ahmad ya jaddada goyon bayan Birtaniya na barin ikon wurare masu alfarma a birnin Kudus a karkasin ikon kasar Jordan.

“Hakika babbar alfarma ce kasancewa a Masallacin Kudus a wannan safiyar (Alhamis) tare da Daraktan Sashen Wakafi na Birnin Kudus, Sheikh Azzam al-Khatib,” kamar yadda ya wallafa a shafinsa na Twitter.

A halin yanzu, an cimma yarjejeniyar cewa Musulmi za su ci gaba da ibada a Masallacin Kudus, yayin da mabiya sauran addinin ke iya kai ziyara a Masallacin, wanda shi ne na uku wajen matsayi ga Musulumi — Yahudawa kuma na daukar sa a matsayin ainihin wurin bautarsu.

Minista Ahmad ya kuma ziyarci binin Hebron da ke Gabar Yammacin Kogin Jordan, bayan a ranar Laraba ya gana da Ministan Harkokin Wajen Isra’ila, Eli Cohen a Yammacin Birnin Kudus.

Daga nan ya je birnin Ramallah da ke Yammacin Kogin Jordan, suka gana da Ministan Harkokin Wajen gwamnatin Falasdinu, Riyad al-Maliki.

A shekarar 1967 ne Isra’ila ta mamaye Gabashin Kusu a lokacin yakinta da kasashen Laraba, kafin a 1980 ta mayar da yankin karkashin ikonta, matakin da kasashen duniya ba su amince da shi ba.

An kama mutum uku da ƙwato wayoyin lantarki na sata 

Zan ci gaba da bada kuɗin hadaya kyauta — Gwamna Zulum 

Obasanjo na yunƙurin ɓata min suna don ɗan takararsa — Atiku

Sojoji sun kama masu garkuwa da mutane a Yobe