Ministar kudi, Kemi Adeosun ta yi murabus
Rahotanni na bayyana cewa, Ministar kudin Najeriya Kemi Adeosun ta yi murabus daga mukaminta a yau Juma’a. Sai dai ba a bayyana ko takardar murabus din nata ya kai ga Shugaba Buhari ba. Rahotan na bayyana cewa, Kemi Adeosun ta yi murabus ne bisa ga zargin samun takardar yi wa kasa hidima NYSC na bogi […]

Rahotanni na bayyana cewa, Ministar kudin Najeriya Kemi Adeosun ta yi murabus daga mukaminta a yau Juma’a.
Sai dai ba a bayyana ko takardar murabus din nata ya kai ga Shugaba Buhari ba.
Rahotan na bayyana cewa, Kemi Adeosun ta yi murabus ne bisa ga zargin samun takardar yi wa kasa hidima NYSC na bogi da kuma matsa mata lamba akan batun.
Cikakken rahoton na nan tafe.