Ministar Mata na rokon addu’a bayan ta harbu da COVID-19

Pualine Tallen ta killace kanta, tana rokon addu’o’i daga jama’a

Ministar Mata na rokon addu’a bayan ta harbu da COVID-19

Ministar Harkokin Mata, Pauline Tallen

Ministar Harkokin Mata ta Najeriya, Pauline Tallen ta harbu da cutar COVID-19.

Ministar da kanta ta sanar da kamuwar ta da COVID-19 ta wata sanarwa a safiyar Asabar, inda ta ce tuni ta killace kanta domin jinya.

“Ina sanar da al’umma cewa bayan an yi min gwaji tare da iyalaina, sakamakon nawa ya nuna na harbu da cutar amma iyalaina ba su da ita.

“A halin yanzu dai alamun cutar ba su bayyana a zahiri ba a tare da ni, ammana killace kaina domin jinya,” inji ministar.

Ta ce bayan ta yi hulda da wasu mutane masu COVID-19 da alamarta ba ta nunawa a jikinsu ne likitocinta suka shawarce da ta yi gwajin cutar tare da killace kanta domin tantace matsayin lafiyarta.

Pauline Tallen ta ce bayan an yi an yi hakan ne aka yi musu gwajin da sakamakon nata ya nuna tana dauke da kwayoyin cutar.

Ministar ta roki ’yan Najeriya da su sanya ta a cikin addu’o’insu tare da kiran su da su rika kiyaye matakan kariyar cutar domin hana yaduwarta.

Sojoji sun kashe kwamandan ’yan bindiga da tarwatsa 300

Zaɓen 2027: Tinubu ya sake tsayar da Shettima mataimakinsa

Tinubu ya gaji yana buƙatar ya huta — Peter Obi

Ɗalibai da malamai da aka sace a Oyo sun kuɓuta