Morocco ta kori Najeriya daga AFCON

A ranar Lahadi ne Morocco za ta yi karon-batta a wasan ƙarshe da Senegal.

Morocco ta kori Najeriya daga AFCON

Tawagar ƙwallon ƙafar Morocco ta kori Najeriya daga Gasar Kofin Nahiyar Afirka (AFCON) bayan doke ta a wasan kusa da na ƙarshe da suka fafata a yammacin ranar Laraba.

Morocco wadda ita ce mai masaukin baƙi ta doke Najeriya ne a bugun fanareti da ci 4–2, bayan an buga minti 120 babu ci, lamarin da ya ba ta nasarar tsallakawa zuwa wasan ƙarshe na gasar.

A ranar Lahadi ne Morocco za ta yi karon-batta a wasan ƙarshe da Senegal, wadda ita ma doke Masar da ci 1-0 a ɗaya wasan kusa da na ƙarshe da suka fafata.

An sanya dokar hana fita a wasu yankunan Taraba

Jami’an NSCDC sun daƙile harin ’yan bindiga a Kano

Matsalar Tsaro: Ku sayi makamai don kare kanku — Sarkin Argungun

Mai juna biyu na wata 8 ta shigar da ƙarar neman saki