Mun bankado sunan jariran da ake biya albashi daga lalitar Borno – Zulum
Ya ce an gano hakan ne bayan aikin tantance ma’aikatan da aka yi.
Babagana Umara Zulum, Gwamnan Jihar Borno
Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya ce an bankado sunan jarirai a jerin wadanda ake biya albashi daga lalitar Jihar.
Ya ce an gano sunayen ne a Karamar Hukumar Shani ta Jihar, bayan aikin tantance ma’aikata a Jihar.
- ‘’Yan bindiga suna aikata ta’addanci amma ba a ’yan ta’adda ba ne’
- Yadda siyasa take hana Kano ci gaba
Ana dai zargin cewa wasu jami’an gwamnati ne ke wawure albashin ma’aikatan bogin da ake da su a fadin Jihar.
Ya bayyana hakan ne yayin bikin al’adu na Menwara a garin Shani, ranar Asabar.
Gwamna Zulum ya ce tun da farko an kirkiro shirin tantance ma’aikatan ne domin gano na bogi daga cikinsu, amma masu adawa da hakan a Karamar Hukumar suka shirya zanga-zangar rashin nuna goyon baya.
Ya ce, “Ina sanar da ku cewa bayan kammala tantancewar, mun bankado sunayen jarirai a jerin ma’aikata, yayin da muka kuma gano cewa a duk wata, akan kashe Naira miliyan 19 wajen biyan ma’aikatan bogi a kowanne wata a Karamar Hukumar Shani.
“Akwai iyali daya da muka gano sunan ma’aikatan bogi 300. Ina fargabar in hakan ya ci gaba, akwai yiwuwar Karamar Hukumar ta gaza biyan albashi a nan gaba kadan,” inji Gwamnan.
Ya kuma yi zargin cewa guraben ayyukan da ya kamata a ba mutanen Karamar Hukumar ana sayar wa wasu akan N250,000, lamarin da ya ce yana hana matasan da suka yi karatu samun aiki.