Mutane miliyan 50 suka yi gudun hijira saboda rikici a bara – Rahoto

kungiyar kare hakkin dan Adam mai suna Amnesty International ta ce mutane miliyan 50 ne suka yi gudun hijira a bara saboda rikice-rikicen da suka dabaibaye duniya. kungiyar ta bayyana shugabannin duniya sun yi abin kunya da alla-wadai wajen yaki da kungiyar ISIL a Iraki, inda suka gaza kare fararen hula daga ayyukan kungiyar.Sakataren kungiyar […]

Mutane miliyan 50 suka yi gudun hijira saboda rikici a bara – Rahoto
Mutane miliyan 50 suka yi gudun hijira saboda rikici a bara – Rahoto

kungiyar kare hakkin dan Adam mai suna Amnesty International ta ce mutane miliyan 50 ne suka yi gudun hijira a bara saboda rikice-rikicen da suka dabaibaye duniya.

kungiyar ta bayyana shugabannin duniya sun yi abin kunya da alla-wadai wajen yaki da kungiyar ISIL a Iraki, inda suka gaza kare fararen hula daga ayyukan kungiyar.
Sakataren kungiyar Amnesty, Salil Shetty ne ya bayyana haka a shekaranjiya Laraba a lokacin da yake karanta rahoton da kungiyarsu ta fitar kan ayyukan keta hakkin dan Adam a duniya.
A rahoton mai dauke da shafi 415 da ya yi cikakken bayani kan yadda ake keta hakkin bil Adama a kasashe 160, ya zargi shugabannin duniya da yin sakaci wajen kare fararen hula.
kungiyar ta bayyana abin kunya ne idan aka duba yadda duniya take kawar da ido kan irin yadda hukumomi da ’yan bindiga suke cin zarafin fararen hula, inda aka bar mutane cikin ukuba ba tare an yi dauki kwakkwaran mataki ba.
Rahoton kungiyar ya bukaci hukumomi su bi yarjejeniyar da aka cimma a bara da ta yi bayanin yadda za a rika sayen makamai da kuma sayarwa.
kungiyar ta ce idan aka bi yarjejeniyar sau-da-kafa, hakan zai sanya a daina dakon makamai don kai su kasashe irinsu Siriya da Iraki.
Susanna Flood, Daraktar watsa labarai ta kungiyar ta shaida wa kafar yada labarai ta Al Jazeera cewa: “Akalla mutane kimanin rabin miliyan sukan mutu kowace shekara, inda miliyoyi sukan samu raunika ko a yi musu fyade ko kuma a tilasta musu yin gudun hijira, wanda hakan ya samu nasaba ne wajen takaita cinikayyar makamai da harsasai. Ana yin cinikayyar makamai cikin sirri ne.”
Rahoton ya kuma bayyana: “Ana kashe Dala biliyan 100 kowace shekara wajen cinikayyar makamai. Kodayake 10 daga cikin dilolin da suke safarar makamai sun amince da yarjejeniyar sayar da makamai da aka cimma bara. Amma Amurka da Isra’ila har yanzu ba su fara amfani da yarjejeniyar ba. Har yanzu kasashe kamar China da Kanada da Rasha ba sa bin yarjejeniyar sau-da-kafa.”
Rahoton ya bayyana wadanda rikice-rikice ya raba da gidajensu a bara yawansu ya kai miliyan 50, karo na farko ke nan tun bayan yakin duniya na biyu.
Amnesty ta dora alhakin hakan a kan bangaren tsaro na Majalisar dinkin Duniya, sannan ta yi hasashen al’amarin zai yi kamari a wannan shekarar matukar ba a shawo kan zirga-zirgar makami ba.