Mutum 900 sun warke daga COVID-19 a Legas
Mutanen da sauka warke daga annobar coronavirus sun kai 908 bayan an sallami karin mutum 33 a jihar Legas. Gwamnan jihar Legas Babajide Sanwo-Olu ya sanar da haka bayan sallamar karin mutum 33 a jihar ranar Talata. 30 daga cikin wadanda aka sallama ‘yan Najeriya ne, sauran ukun kuma ‘yan kasar Indiya. Coronavirus: Adadin wadanda […]
Daga tsakiya a can kuryar, gwamnan jihar Legas Babajide Sanwo-Olu tare da jami’an kiwon lafiya a sabuwar cibiyar killace masu coronavirus ta Oniru a Legas
Mutanen da sauka warke daga annobar coronavirus sun kai 908 bayan an sallami karin mutum 33 a jihar Legas.
Gwamnan jihar Legas Babajide Sanwo-Olu ya sanar da haka bayan sallamar karin mutum 33 a jihar ranar Talata.
30 daga cikin wadanda aka sallama ‘yan Najeriya ne, sauran ukun kuma ‘yan kasar Indiya.
- Coronavirus: Adadin wadanda su ka kamu a Najeriya ya haura 10,000
- Abubuwa bakwai da ba ku sani ba game da ayyukan NCDC
Zuwa yanzu jihar Legas ita ce kan gaba a fadin Najeriya da masu cutar COVID-19 5,277.