Mutuwar Almajirai: Tinubu ya buƙaci a samar da matakan kare ɗalibai

Aƙalla almajirai 17 ne suka rasu, yayin da wasu bakwai suka jikkata a gobarar.

Mutuwar Almajirai: Tinubu ya buƙaci a samar da matakan kare ɗalibai

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci hukumomin ilimi su tabbatar da cewa makarantun gwamnati da masu zaman kansu sun ɗauki matakan kare ɗalibai daga haɗura.

Wannan kira na zuwa ne bayan da wata gobara ta yi ajalin almajirai 17 a wata makarantar tsangaya da ke garin Ƙauran Namoda, a Jihar Zamfara.

Gobarar, wacce ta tashi da daddare a ranar Talata, ta kuma jikkata wasu almajirai bakwai, amma yanzu haka suna asibiti ana kula da su.

Shugaba Tinubu ya jajanta wa Gwamnatin Jihar Zamfara da iyalan waɗanda da suka rasa ’ya’yansu a wannan iftila’in, tare da yin addu’ar samun sauƙi ga waɗanda suka jikkata.

Ya buƙaci makarantu da su fifita tsaro da kula da lafiyar ɗalibai a kowane lokaci.

A yayin bincike, rundunar ‘yan sandan Zamfara ta ce tana ƙoƙarin gano musabbabin tashin gobarar.

Majalisar wakilai ta dakatar da CBN daga ƙara kuɗin cajin ATM

Hanyoyi 6 da mutum zai kare kansa daga tsananin zafi

’Yan sanda sun ceto mutum 30 daga hannun ’yan bindiga a Katsina

Ba abin da zai faru idan aka tsige Fubara – Wike