NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa Ake Hana ’Yan Najeriya Fadin Albarkacin Bakinsu
Shirin Najeriya A Yau zai yi duba a kan tanade-tanaden doka a kan ’yancin faɗin albarkacin baki a Nijeriya. Shin me ya sa ake hana ’yan ƙasar faɗin albarkacin bakinsu?

Wasu matasan Najeriya a lokacin wata zanga-zanga a kan titin Legas-Ibasan kan cin zalinsu da ‘yan sanda ke yi. (Hoto:PIUS UTOMI EKPEI / AFP) (Photo by PIUS UTOMI EKPEI/AFP via Getty Images)
Sashe na 4 na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya na ɗauke da tanade-tanade musamman da suka shafi ’yancin ɗan Adam a dokar Najeriya.
Cikin tanade-tanaden akwai ’yancin da doka ta bai wa kowane ɗan Nijeriya na rayuwa da shiga taro da kuma faɗin albarkacin baki.
- NAJERIYA A YAU: ‘Karambanin’ Malamai kan ƙudurorin Harajin Tinubu
- DAGA LARABA: Abin ya sa ’yan Nijeriya ke kishin ƙabila fiye da ƙasa
Shirin Najeriya A Yau zai yi duba a kan tanade-tanaden doka a kan ’yancin faɗin albarkacin baki.
Domin sauke shirin, latsa nan