NAJERIYA A YAU: Hukuncin Dauri Kafin A Rataye Abdulmalik Bai Mana Ba —Dangin Hanifah
Dangin Hanifah, wadda malaminta, Abdulmalik Tanko, ya sace sannan ya kashe ta suna so a gaggauta aiwatar da hukuncin rataya da aka yanke mishi
Abdulmalik Tanko tare da sauran mutum biyu da ake tuhuma da kisan Hanifa
Domin sauke shirin latsa nan
Iyayen karamar yarinyar nan Hanifa Abubakar, wadda malaminta ya sace sannan ya kashe ta a Kano, sun ce ba su gamsu da hukuncin daurin shekara biyar kafin a zartar mishi da hukuncin rataya ba.
A ranar 28 ga watan Yulin shekarar 2022 kotu ta yanke wa Abdulmalik Tanko da abokinsa wurin kisan Hanifa hukuncin dauri a gidan gyaran hali da kuma kisa ta hanyar rataya bayan sun cinye wa’adin da aka diba musu.
- DAGA LARABA: Daga Lahadin Nan INEC Za Ta Rufe Rajistar Katin Zabe
- NAJERIYA A YAU: Matsalar Tsaro Za Ta Iya Kawo Wa Zaben 2023 Cikas
Wannan hukunci, da aka yanke bayan wata shida ana shari’ar kisan na ci gaba da samun sharhi daga bakin jama’a, ciki har da dangin Hanifa, wadda Abdulmalik Tanko ya halaka.
Shirin Najeriya A Yau ya tattauna da Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano da kuma dangin marigayiya Hanifa kan wannan hukunci. A yi sauraro lafiya: