NAJERIYA A YAU: Irin Asarar Da Aka Tafka A Kasuwar Kafintoci Da Ke Kano

Wannan gobara da ba a san musabbabinta ba, ta janyo asarar miliyoyin Naira tare da jefa waɗanda abin ya shafa cikin mawuyacin hali.

NAJERIYA A YAU: Irin Asarar Da Aka Tafka A Kasuwar Kafintoci Da Ke Kano

Gobara a irin wannan yanayi  na iska musamman a kasuwanni da gidaje ba sabon abu ba ne kuma ba abun mamaki ba.

Wasu kafintoci da ke aiki a Kasuwar Lale da ke unguwar Tal’udu a Ƙaramar Hukumar Gwale da ke Jihar Kano sun wayi gari da alhinin gobarar da ta yi sanadiyyar raba su da hanyar abincinsu.

Wannan gobara da ba a san musabbabinta ba, ta janyo asarar miliyoyin Naira tare da jefa waɗanda abin ya shafa cikin mawuyacin hali.

Ko wane irin hasara aka yi a wannan gobara?

Wannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan