NAJERIYA A YAU: Matakan daƙile kisan matafiya a hanyoyin Najeriya

A kwanakin baya ma an kashe wasu matafiya a garin Uromi da ke jihar Edo a hanyar su ta komawa Kano

NAJERIYA A YAU: Matakan daƙile kisan matafiya a hanyoyin Najeriya

Matsalar tare fasinjoji da kashe su a hanyoyin Najeriya na ƙara tsananta, musamman a yankunan Arewa.

Misali, a shekarun baya an sha tare matafiya a kashe su a hanyar Abuja zuwa Kano. A kwanakin baya ma an kashe wasu matafiya a garin Uromi da ke jihar Edo a hanyar su ta komawa Kano.

Sai na kwanan nan da ya faru a Jihar Filato inda aka kashe wasu matafiya da ke kan hanyarsu ta zuwa ɗaurin aure.

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne da nufin gano matakan daƙile afkuwar haka a nan gaba.

Domin sauke shirin, latsa nan