NAJERIYA A YAU: Cushe-cushen Da Ake Zargin An Yi A Sabbin Dokokin Haraji
A ɗaya ɓangaren kuma, Fadar Shugaban Ƙasa ta yi nuni da cewa abin da aka yi gyara ne na fasaha da tsari, ba sauya ma’anar doka ba.
Hukumar Tara Kudin Shiga ta Tarayya (FIRS) ce ke karbar haraji a madadin Gwamnatin Tarayya
Takaddama mai zafi ta dabaibaye sabbin dokokin haraji da Majalisar Dokoki ta Ƙasa ta amince da su, bayan zarge-zargen cewa an yi sauye-sauye a cikin dokokin ta bayan fage, bayan an kammala dukkan matakan amincewa da su a majalisa.
Batun da ya taso ya jawo cece-kuce daga ’yan majalisa, jam’iyyun adawa da ƙungiyoyin fararen hula, inda suke tambayar sahihancin abin da aka miƙa wa Fadar Shugaban Kasa domin aiwatarwa.
Masu suka na cewa sauye-sauyen da ake zargin an yi ba tare da amincewar majalisa ba na iya lalata tsarin dimokuraɗiyya, tare da haifar da rashin gaskiya da riƙon amana a tsarin dokoki.
A ɗaya bangaren kuma, Fadar Shugaban Ƙasa ta yi nuni da cewa abin da aka yi gyara ne na fasaha da tsari, ba sauya ma’anar doka ba.
Ko waɗanne irin sauye-sauye aka yi wa sabuwar dokar harajin?
- NAJERIYA A YAU: Irin Asarar Da Aka Tafka A Kasuwar Kafintoci Da Ke Kano
- DAGA LARABA: Yadda Ragin Farashin Man Fetur Zai Shafi Rayuwar ‘Yan Najeriya
Wannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.
Domin sauke shirin, latsa nan