Najeriya A Yau: Yadda jami’ai ke ‘agaza wa’ masu fasa-kwauri
Fasa-kwauri na cikin dalilan da ke kassara tattalin arzikin kasa
Domin sauke shirin latsa nan.
Ga alama kwalliya ba ta biyan kudin sabulu bayan da aka rufe iyakokin Najeriya da nufin hana fasa-kwauri.
Hasali ma, jami’an da aka dora wa alhakin kula da iyakokin ake zargi da taimaka wa masu fasa-kwaurin, lamarin da ke haddasa nakasu ga tattalin arzikin Najeriya.
Wannan shirin na Najeriya a Yau ya yi nazari a kan wannan batu.