NAJERIYA A YAU: Yadda Kabilanci Ke Neman Hana Banki Gina Kasuwar Taminus Ta Jos

Asarar da ake tafkawa a dalilin  rashin Kasuwar Taminus da hujjar masu son hana Bankin Jaiz sake gina ta

NAJERIYA A YAU: Yadda Kabilanci Ke Neman Hana Banki Gina Kasuwar Taminus Ta Jos

Wani bangare na Kasuwar Terminus da ke Jos

Domin sauke shirin kai tsaye, latsa nan.

Yunkurin wasu kungiyoyi na hana Bankin Jaiz sake gina Kasuwar Taminus da ke Jos a Jihar Filato ya bar baya da kura.

Rahotanni sun bayyana cewa kasuwar da ake takaddamar sake ginawa ita ce ginanniyar kasuwa  mafi girma a Afirka ta Yamma.

Shin me ya sa kungiyoyin ba sa so a  sake gina kasuwar?

Shirinmu na yau ya binciko irin asarar da ake tafkawa a dalilin  rashin kasuwar da ma wasu batutuwa.