NAJERIYA A YAU: Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen Malabu

Yadda baƙuwar cutar take yaɗuwa da matakan da ya kamata a ɗauka don kauce wa kamuwa da ita.

NAJERIYA A YAU: Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen Malabu

Wata cuta mai cin naman jikin dan Adam ta yi sanadin mutuwar mutum takwas yayin da wasu fiye da 60 suke kwance a asibiti a garin Malabu da ke Karamar Hukumar Fufure ta Jihar Adamawa.

Wannan lamari dai ya jefa fargaba a zukatan mazauna yankin.

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi bincike a kan yadda wannan cuta take yaɗuwa da matakan da ya kamata a ɗauka don kauce wa kamuwa da ita.

Domin sauke shirin, latsa nan