NAJERIYA A YAU: Yadda ’Yan Bindiga Suka Yanka ’Yan Kasuwa A Jihar Neja
Haƙiƙanin abun da ya faru a Kasuwar Daji, inda ’yan ta’adda suka yi wa mutane yankan rago a Ƙaramar Hukumar Borgun Jihar Neja,
Harin da wasu ’yan ta’adda suka kai kasuwar Daji da ke Ƙaramar Hukumar Borgu a Jihar Neja ya sake jawo hankalin al’umma kan matsalar rashin tsaro da ke kara ta’azzara a yankunan karkara a shiyyar Arewa ta Tsakiya.
Kasuwar Daji, wadda ke zama cibiyar hada-hadar kasuwanci ga manoma, ’yan kasuwa da mazauna ƙauyuka maƙwabta, ta kasance wuri na zaman lafiya kafin wannan mummunan lamari da ya girgiza mazauna yankin.
Batutuwa da dama daga kafafen yaɗa labarai da dama sun bayyana mabanbantan ra’ayoyi kan batun.
Ko mene ne haƙiƙanin abin da ya faru a wannan hari da ’yan bindiga suka kai a kasuwar Daji?
- NAJERIYA A YAU: Yadda Ya Kamata Ku Gudanar Da Rayuwa A Shekarar 2026
- DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Matan Wannan Zamanin Ba Sa Son Talaka
Wannan shi ne batun da shirin Najeriya a yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.
Domin sauke shirin, latsa nan