Najeriya A Yau: Za A Kashe Duk Wanda Ya Saci Mutum A Filato
Abin da doka ta ce kan halaccin kashe wanda bai aikata kisa ba.
Za’a Kashe Duk Wanda Ya Saci Mutum A Jos
Domin sauke shirin latsa nan
A yunkurinta na dakile ayyukan masu garkuwa da mutane da ya fara yawaita a kwanan nan, Gwamnatin Jihar Filato ta kara jaddada kudirinta na kashe duk wanda aka tabbatar ya saci wani domin karbar kudin fansa.
Anya zai yiwu kuwa? Me doka ta ce dangane da kashe wanda bai aikata kisa ba?
Mun tattauna da gwamnatin jihar domin sanin yadda za a gudanar da wannan hukunci, mun kuma ji ta bakin wani masanin shari’a game da halaccin wannan doka.