Najeriya da Pakistan sun yi taron bunkasa cinikin magunguna
An gudanar da taron yini biyu tsakanin masu sarrafa magunguna na Najeriya da takwarorinsu na kasar Pakistan a birnin Ikko domin samar da hanyoyin bunkasa harkokin samar da magunguna a Najeriya, cikin sauki kuma ingantattu.Da yake jawabin wajen taron, daya daga cikin shugabannin taron, Alhaji Ibrahim Ahmed Yakasai ya ce an zabi kasar Pakistan ne […]

An gudanar da taron yini biyu tsakanin masu sarrafa magunguna na Najeriya da takwarorinsu na kasar Pakistan a birnin Ikko domin samar da hanyoyin bunkasa harkokin samar da magunguna a Najeriya, cikin sauki kuma ingantattu.
Da yake jawabin wajen taron, daya daga cikin shugabannin taron, Alhaji Ibrahim Ahmed Yakasai ya ce an zabi kasar Pakistan ne domin yin wannan hulda saboda tana daya daga cikin kasashen duniya da ke da kwarewa wajen sarrafa magunguna, musammam a yankinsu na Asiya, kana suna da yanayi irin na Najeriya.
Alhaji Yakasai ya ce yanzu haka Najeriya da kasar Pakistan suna kasuwancin da yake da adadin Dala miliyan 100, wanda ganin ya yi kadan ya sa aka shirya taron na yini biyu domin a kara shi, musamman ta hanyar sarrafa magunguna.
Ya ce wannan taron shi ne harsashin matakin habako da masana’antun magunguna na gida ta yadda wadanda suka durkushe za su samu abokan hulda da za su tado su kuma ana sa ran wannan taron ya samar da karin aikin yi ga ’yan Najeriya.
Da kuma ya tabo batun tsaro, musammam a kan yadda ba za su fada mugun hannu ba, sai Alhaji Ibrahim ya ce sun cimma matsaya game da wannan. Ya ce don haka ne ma ya sa gwamnati ta kawo jami’an tsaro cikin batun, musammam masu nasaba da shiga da ficin kayayyaki da mutane, tare da hukumomin da ke da hannu wajen ingancin abinci da magunguna da kuma duk wani mai ruwa da tsaki a harkar tsaron abinci da kaya da mutane.
Da wakilin Aminiya ya tambayi daya daga cikin mahalarta taron, Malam Ahmed Salim abin da ya ba shi kwarin gwiwar zuwa, sai ya ce, “Najeriya kasa ce da ke da dimbin albarka, kana tana da wadatacciyar kasuwa da wajen sarrafa duk abin da mutum ke so, kuma ba zai yi da-na-sani ba”.
Ana sa ran samun masu sarrafa magunguna a nan cikin gida da kuma can kasar Pakistan din, kuma suna da damar shigowa da su nan Najeriya.