Najeriya na shirin kwashe ’yan ƙasarta daga Lebanon

Aƙalla ’yan Najeriya 5,000 ke zaune a ƙasar Lebanon inda ake zargin yiwuwar ɓarkewar yaƙi.

Najeriya na shirin kwashe ’yan ƙasarta daga Lebanon

Smoke billows from the site of an Israeli air strike in the Lebanese village of Khiam, near the Lebanon-Israel border, on September 23, 2024. The Israeli military on September 23 told people in Lebanon to move away from Hezbollah targets and vowed to carry out more “extensive and precise” strikes against the Iran-backed group. (Photo by Rabih DAHER / AFP) (Photo by RABIH DAHER/AFP via Getty Images)

Gwamnatin Najeriya ta ba da umarnin kwaso ’yan ƙasarta daga ƙasa Lebanon sakamakon fargabar yaƙi.

Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya ta buƙaci ’yan ƙasar mazauna Lebanon da su garzaya ofishin jakadanci da ke Lebanon domin ɗaukar bayansu da kuma kwaso su zuwa gida.

An fara fargabar ɓarkewar yaƙi tsakanin Isra’ila da Iran ne bayan harin makamai masu linzami sama da 180 da Iran kai wa Isra’ila.

Iran ta kai harin ne a matsayin martani kan kisan shugabannin ƙungiyar Hisbullah da hare-haren Isra’ila suka kashe a Lebanon.

Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya lashi takobin ɗaukar fansa, a yayin da Iran ta ce ta shirya, lamarin da ya sa ake fargabar ɓarkewar mummunan yaƙi a yankin Gabas ta Tsakiya.

Ƙasashen Saudiyya da China dai sun buƙaci manyan abokan gaban da su kai zuciya nesa.

Shin Binani ta dawo?

Sana’ar Bola-jari: Muna taka sawun barawo — Shugaban ‘yan gwangwan

’Yan sanda sun ƙwace sakamakon zaɓe a Ribas

Yadda mutanen Jigawa suka ƙi fita zaɓen ƙananan hukumomi