Najeriya ta ƙara kuɗin yin takardar fasfo

An ƙara kuɗin mallakar fasfon ne a gida Najeriya kaɗai, bai shafi masu yi a kasashen waje ba

Najeriya ta ƙara kuɗin yin takardar fasfo

Fasfo

Gwamnatin Najeriya ta sanar da kara kuɗin mallakar takardar fasfo tafiye-tafiye da kashi 43%.

Hukumar Shige da Fice ta bayyana cewa an ƙara kuɗin mallakar fasfon a gida Najeriya ne kawai, bai shafi masu yi a kasashen waje ba.

Sanarwar da kakakin hukumar, Kenneth Udo, ya fitar ta ce takardar fasfo mai shafi 64 ya tashi daga N75,000 ya koma N100,000.

Fasfo mai shafuka 32 kuma an ƙara kudin mallakarsa daga Naira dubu 35 zuwa Naira dubu 50.

Sanarwar ta ranar Laraba ta ce sabon farashin zai fara aiki ne daga ranar 1 ga watan Satumba, 2024.

A cewarsa, an ƙara kuɗin mallakar fasfo ɗin ne da sun kara ingancinsa da nagaratarsa.

Kashim Shettima zai jagoranci tawagar Nijeriya a taron MDD

NECO ta fitar da sakamakon jarrabawar 2024

Kano: Abba ya rusa ciyamomin riko

An haramta wa ma’aikatan Asibitin Tarayya yin ‘kirifto’ a wurin aiki

Tags