Najeriya ta koma ta 31 a jadawalin FIFA

Najeriya ta fara wannan shekarar ne a ta 32.

Najeriya ta koma ta 31 a jadawalin FIFA

Kungiyar Kwallon Kafan Super Eagles

Najeriya ta koma ta 31 a jerin kasashe mafi kwarewa a kwallon kafa da Hukumar Kwallon Kafa ta Duniya fitar.

Hakan na zuwa duk da tawagar ta Super Eagles ta lallasa Sao Tome and Principe da ci 10-0, a wasan share fage na gasar cin Kofin Afirka.

Sai dai Super Eagles wadda ta nada sabon koci, Jose Peseiro ta ci gaba da zama ta hudu a Afirka.

Najeriya ta fara wannan shekarar ne a ta 32, inda ta samu ci gaba bayan da ta dawo na 30 a watan Maris, kafin ta kara sauka zuwa ta 31 a jadawalin na FIFA.

Senegal wadda ita ce ta daya a Afrika ta dawo ta 18 a teburin duniya, daga ta 22 a watan Maris.

Sai dai Brazil ta kara bai wa Belgium rata a matsayin ta daya, yayin da Argentina ta sauko da Faransa daga ta uku.

An sanya dokar hana fita a wasu yankunan Taraba

Jami’an NSCDC sun daƙile harin ’yan bindiga a Kano

Matsalar Tsaro: Ku sayi makamai don kare kanku — Sarkin Argungun

Mai juna biyu na wata 8 ta shigar da ƙarar neman saki