Najeriya ta lallasa Saliyo da ci 2-1

Ana buga wasan ne don neman cancanta buga Kofin Nahiyar Afirka

Najeriya ta lallasa Saliyo da ci 2-1

Tawagar Super Eagles

Kungiyar kwallon kafar Najeriya ta Super Eagles ta lallasa takwararta ta Leone Stars ta kasar Saliyo da ci 2-1 a filin wasa na Moshood Abiola da ke Abuja.

An dai fafata wasan ne don neman gurbin cancanta buga Kofin Nahiyar Afirka (AFCON).

Dan wasa Jonathan Morsay ne ya ci kwallo ta farko a minti na 11 da fara wasan, amma dan wasan tsakiya da ke wasa a kungiyar Everton, Alex Iwobi ya sake jefa wa Najeriya kwallo ta biyu a minti na 16.

Da wannan nasarar dai, yanzu Najeriya ce ta biyu a rukunin ‘A’, inda take da maki uku daga wasa daya.

Kasar Gini Bisau ce dai a saman teburin rukunin su ma da maki uku, kodayake su kwallo biyar suka ci a wasan da suka doke Sao Tome and Principe, wanda aka tashi 5-1.

 

 

 

An sanya dokar hana fita a wasu yankunan Taraba

Jami’an NSCDC sun daƙile harin ’yan bindiga a Kano

Matsalar Tsaro: Ku sayi makamai don kare kanku — Sarkin Argungun

Mai juna biyu na wata 8 ta shigar da ƙarar neman saki