Namadi ya kaddamar da sabbin jiragen kasa a Legas

Gwamnatin tarayya ta kaddamar da jiragen kasa da taragai 60 masu na’ura  mai  sanyaya daki a Ikko,  wadanda za su  rika aiki cikin birnin da kuma wanda  zai  rika zuwa  Kano.Da yake  jawabi  wajen  kaddamar da jiragen, mataimakin shugaban kasa, Akitek Namadi Sambo ya ce  yana  fata  nan ba da  jimawa  ba  gwamnati  za ta  […]

Namadi ya kaddamar da sabbin jiragen kasa a Legas
Namadi ya kaddamar da sabbin jiragen kasa a Legas

Gwamnatin tarayya ta kaddamar da jiragen kasa da taragai 60 masu na’ura  mai  sanyaya daki a Ikko,  wadanda za su  rika aiki cikin birnin da kuma wanda  zai  rika zuwa  Kano.
Da yake  jawabi  wajen  kaddamar da jiragen, mataimakin shugaban kasa, Akitek Namadi Sambo ya ce  yana  fata  nan ba da  jimawa  ba  gwamnati  za ta  samu  damar karo  jiragen  domin ingata  harkokin sufuri  a  cikin kasa, lamarin da zai  kara inganta  hanyoyin motoci  a duk  fadin tarayyar  Najeriya.
Mataikmakin shugaban kasa  ya ce  yana  fata ’yan Najeriya  za su  kula da jiragen tamkar nasu  kuma za a yi  amfani  da su ta yadda ya dace.
Shi ma ministan sufuri, Sanata Idris Umar ya ce baya ga jiragen, wadanda sun yi  daidai da duk wani jirgin kasa da za a iya amfani  duk duniya, gwamnati ta kusan kammala gyara  daukacin hanyoyin jirgin kasa da ke fadin tarayyar Najeriya.
Shi ko  manajan darekatan  hukumar,  Injiniya  Sijuwade  ya ce  yana  taya ’yan Najeriya murnar samun  wadannan jiragen kuma fatarsa ita ce  a  samu a kara sawo wasu.  Ya  ba ’yan Najeriya tabbacin hukumarsa za ta kula da su yadda ya dace, kodayake ya bukaci taimakon ’yan Najeriya a kan haka.
Jim kadan da kaddamarwar, mataimakin shugaban kasa  da  minista  da  sauran manyan  jami’an gwamnati  sun shiga jirgi guda, wanda  zai yi  aiki  cikin Legas  daga  tashar Iddo terminus  zuwa Ikeja,  inda  daga  nan ne mataimakin shugaban kasa ya koma  Abuja.