NDLEA ta lalata tan 24 na miyagun kwayoyi a Kwara
Kwamandan NDLEA a jihar, Ibrahim Saidu, ya ce, sun gurfanar da dillalan miyagun kwayoyi su 171 a Jihar Kwara a cikin wannan shekara.
Yayin lata miyagun kwayoyi
Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA), ta lalata miyagun kwayoyi da nauyinsu ya kai tan 24.6 da ta kama a Jihar Kwara.
Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN), ya ce, a ranar Laraba NDLEA ta yi wannan aikin ne a Ilorin.
- Mutum 61 sun mutu a hadurra a Borno —Hukuma
- NAJERIYA A YAU: Matsayin Kuri’ar ’Yan Gudun Hijira A Zaben 2023
Gwamnan jihar, AbdulRahman AbdulRazaq, ya yaba wa hukumar da wannan nasarar da ta samu a jihar.
AbdulRazaq ya bai wa NDLEA tabbacin gwamnatinsa za ta ci gaba da mara mata baya don ci gaba da aikinta a jihar yadda ya kamata.
A nasa bangaren, Kwamandan NDLEA a jihar, Ibrahim Saidu, ya ce, sun samu nasarar gurfanar da dillalan miyagun kwayoyi su 171 a jihar a cikin wannan shekara.
(NAN)