NLC na shirin fara yajin aiki a Filato

NLC ta ce za ta shiga yajin aikin ne domin gargadi ga Gwamanatin Filato kan ta yi abin da ya kama ce ta game da hakkokin ma’aikata.

NLC na shirin fara yajin aiki a Filato

Kungiyar Kwadago ta Kasa (NLC) da takwararta ta ’yan kasuwa (TUC) a Jihar Filato na shirin fara yajin aikin gargadi na kwana biyar saboda rashin biyan albashi da sauran hakkokin ma’aikata.

Cikin wasikar da ta fitar ranar Alhamis mai dauke da sa hannun shugabanta na jihar, Eugene Manji, NLC ta ce ta soma neman hadin kan sauran takwarorinta a jihar don su shiga yajin aikin.

Shugaban kwamitin sulhu na hadin gwiwa (JNPSNC) reshen Filato, Mista Titus Malau, ya shaida wa NAN cewa shiga yajin aikin ya zama wajibi saboda gazawar gwamnati wajen cimma bukatun ma’aikatanta.

Ya ce matsalar albashin ma’aikata na daga cikin dalilan da suka sanya su yanke shawarar shiga yajin aikin gargadi don jan hankalin gwamnati.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN), ya ce NLC ta shirya fara yajin aikin ne ranar 11 ga Disamba da misalin karfe 12:00 na dare.

Shugabannin kungiyar sun yi kira ga ma’aikatan gwamnati a jihar da su ba da cikakken hadin kansu kan matakin.

 

(NAN)

An yi garkuwa da mutum 43 da kashe yaro a Sakkwato

Klopp zai maye gurbin Nagelsmann a matsayin kocin Jamus

Sojoji sun kama masu ƙera makamai a Kebbi

Bam ya kashe aƙalla mutum shidda a Siriya