NSCDC ta kama matashi kan zargin kona gidaje 4 a Gombe

Matashin ya cinna wa gidajen wuta ne sanadiyyar wani sabani da ya shiga tsakaninsa da wani yayansa.

NSCDC ta kama matashi kan zargin kona gidaje 4 a Gombe

Hukumar Tsaro ta Cibil Difens ta kama wani matashi mai suna Segun Bulus kan zargin kona wasu gidaje guda 4 a garin Dele Jesus da ke Karamar Hukumar Balanga ta Jihar Gombe.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, matashin mai shekaru 27 ya yi wannan aika-aikar ce a daren Talata wayerwar gari Laraba.

Da yake tabbatar da lamarin, Kwamandan hukumar, Muhammad Bello Mu’azu, ya bayyana cewa sun kama matashin ne bayan an soma hatsaniya tsakaninsa da magidanta da ya haddasawa rasa matsugunni.

Hotunan gidajen da matashin ya kona

Kwamanda Mu’azu ya yi karin da cewa tun farko dai matashin ya cinna wa gidajen wuta ne sanadiyyar wani sabani da ya shiga tsakaninsa da wani yayansa.

Kwamandan ya ce suna ci gaba da gudanar da bincike kuma da zarar sun kammala za su tura wanda ake zargin kotu.

Shigo da hatsi daga ƙetare ya karya farashinsa a Neja

Ya yi wa kansa keji don daina shan sigari

Amurka ta dakatar da bai wa Afirka ta Kudu tallafi

Yadda rikicin shugabanci ya janyo rufe babban masallacin gari