NYSC ta kara wa’adin rijistar masu yi wa kasa hidima
Hukumar yi wa kasa hidima ta Najeriya NYSC ta dage wa’adin rijistar masu yi wa kasar hidima a duk sansanin da ake horar da ‘yan NYSC zuwa ranar Asabar 27 ga Oktoba. Musamman sababbi masu yi wa kasar hidima wadanda suka kammala Jami’ar Ilorin. An sanarwa duk shugabannin reshen NYSC na jihohin kasar. Misis R. […]
Hukumar yi wa kasa hidima ta Najeriya NYSC ta dage wa’adin rijistar masu yi wa kasar hidima a duk sansanin da ake horar da ‘yan NYSC zuwa ranar Asabar 27 ga Oktoba. Musamman sababbi masu yi wa kasar hidima wadanda suka kammala Jami’ar Ilorin.
An sanarwa duk shugabannin reshen NYSC na jihohin kasar.
Misis R. B Ohakwu, ce ta rattaba wa sanarwar hannu a madadin Darakta Janar na NYSC Birgediya-Janar Suleiman Kazaure.