Obama zai dakile bazuwar bindigogi a Amurka

Shugaban kasar Amurka Barrack Obama ya zubar da hawaye lokacin da yake jawabi kan yadda iznin mallakar  bindiga ke ci gaba da lakume rayukan Amurkawa.Al’amarin y afaru ne lokacin da yake wa  Amurkawa  jawabi a fadarsa da ke White House, wanda ya samu  halartan ’yan uwan  wadanda  suka yi  hasarar  wasu  nasu sakamakon harbin bindiga […]

Obama zai dakile bazuwar bindigogi a Amurka
Obama zai dakile bazuwar bindigogi a Amurka

Shugaban kasar Amurka Barrack Obama ya zubar da hawaye lokacin da yake jawabi kan yadda iznin mallakar  bindiga ke ci gaba da lakume rayukan Amurkawa.
Al’amarin y afaru ne lokacin da yake wa  Amurkawa  jawabi a fadarsa da ke White House, wanda ya samu  halartan ’yan uwan  wadanda  suka yi  hasarar  wasu  nasu sakamakon harbin bindiga a lokuta daban-daban a baya.
Jawabin Shugaba Obama mai sosa rai  ya caccaki ’yan Majalisar  Dokokin kasar  musammam wadanda suka ki amince da yi wa  dokar mallakar bindiga kwaskwarima. Ya ce Amurkawa  su daure a dauki matakin da suka dace  wajen mallakar bindiga.
Ya ce a kowace shekara kusan Amurkawa dubu 30 ne ke mutuwa  sakamakon harbin bindiga ta hanyoyi kisan  kan mai uwa da wabi, ko kuma masu kashe kansu, ko kuma tashe-tashen hankula  a wajen taro da dai sauran su.
Har ila yau, shugaban ya ce  Amurka ce kasar da ta ci gaba, amma kuma take huskantar hadarin salwantar rayuka ta harbin bindiga, abin da ba a gani  a sauran sassan duniya musammam a cikin kasashen da suka ci gaba.
Shugaban ya bayyana matakai da gwamnati za ta dauka abin da ya kira aiki da hankali. Ya ce zai yi amfani da ikonsa na shugaba mai cikakken iko ba tare da amincewar majalisar dokokin kasar ba, wadda da ta yi ta wa yunkurin kafar angulu wajen yiwa dokar kwaskwarima  musammam ’yan jam’iyyar Republican.
Wasu daga cikin matakan da shugaban ya bayyana  zai dauka  sun hada da tantancewa mai tsauri ga dillalan bindiga su samu karin lasisi. Har ila yau, za a bi dokokin mallakan bindiga sau da kafa sabanin abin da ake da shi yanzu.
Wannan batu  ya janyo muhawara tsakanin Amurkawa kamar yadda wasu suke cewa matakan ba wasu  tasiri za su yi  ba,  kuma  tamkar  karan tsaye ne ga gyaran dokar da majalisar ke yi  wanda ya kai matakin karatu na biyu a zauren majalisar.