Ohinoyi: Sarkin Kasar Ebira ya rasu

Ya koma ga Mahaliccinsa yana da shekaru 94 a duniya, kuma bayan shekaru 25 a kan karagar mulkin Masarautar Ebira

Ohinoyi: Sarkin Kasar Ebira ya rasu

Allah Ya yi Sarkin Kasar Ebira, Ohinoyi Abdul Rahman Ado Ibrahim (CON) rasuwa.

Mai Martaba Abdul Rahman Ado Ibrahim, ya rasu ne a fadarsa da ke garin Okene a Jihar Kogi kafin wayewar garin Lahadi.

Ya koma ga Mahaliccinsa ne yana da shekaru 94 a duniya, kuma bayan shekaru 25 a karagar mulkin Masarautar Kasar Ebira da ke Jihar Kogi.

Ya hau mulki ne a shekarar 1997 bayan rasuwar Ohinoyi Sanni Omolori.

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda

‘Yan bindiga sun ƙone gidan mai da motoci 4 a Enugu

Kwalara ta kashe fiye da mutum 300 a Sudan

Tags