Ohinoyi: Sarkin Kasar Ebira ya rasu

Ya koma ga Mahaliccinsa yana da shekaru 94 a duniya, kuma bayan shekaru 25 a kan karagar mulkin Masarautar Ebira

Ohinoyi: Sarkin Kasar Ebira ya rasu

Allah Ya yi Sarkin Kasar Ebira, Ohinoyi Abdul Rahman Ado Ibrahim (CON) rasuwa.

Mai Martaba Abdul Rahman Ado Ibrahim, ya rasu ne a fadarsa da ke garin Okene a Jihar Kogi kafin wayewar garin Lahadi.

Ya koma ga Mahaliccinsa ne yana da shekaru 94 a duniya, kuma bayan shekaru 25 a karagar mulkin Masarautar Kasar Ebira da ke Jihar Kogi.

Ya hau mulki ne a shekarar 1997 bayan rasuwar Ohinoyi Sanni Omolori.

NNPP ta dakatar da Kawu Sumaila da Ali Madakin Gini

Mun gano inda Bello Turji ya ɓoye —Sojoji

Matar aure ta banka wa mijinta wuta

Abin da ya sa na yi wa Buhari juyin mulki —IBB

Tags