Qatar 2022: ’Yan wasan Iran sun goyi bayan zanga-zangar kin jinin gwamnati
Kyaftin din kungiyar kwallon kafa ta kasar Iran, Ehsan Hajsafi, ya bayyana goyon baya ga masu zanga-zangar adawa da gwamnatin kasarsa.
Kyaftin na Kungiyar Kwallon Kafa ta Iran, Ehsan Hajsafi. (Hoto: France 24).
Kyaftin din kungiyar kwallon kafa ta kasar Iran, Ehsan Hajsafi, ya bayyana goyon baya ga masu zanga-zangar adawa da gwamnatin kasarsa.
Ehsan Hajsafi ya jajanta wa mutanen da suka ji raunuka da iyalan wadanda suka rasu, a jajibirin ranar da kasarsa za ta fafata wasanta da farko da kasar Birtaniya a gasar Kofin Duniya.
- Wike ya gayyaci Kwankwaso bude ayyukan da ya yi a Ribas
- Kaso 60 na ’yan Arewa ba su da asusun ajiya na banki – Uba Sani
Ehsan ya bayyana wa wa taron ’yan jarida cewa masu zanga-zangar, “Su sani cewa muna tare da su, domin abin da ke faruwa a gida babu dadin ji.”
A cewarsa, tawagar kwallon kafar na jajantawa ne a matsayinsu na muryar wadanda ake yi wa danniya a kasar Iran.