Rashin fahimtar juna ke kawo rudani a cikin al’umma – Gwamna Fashola

Gwamnan Jihar Legas, Mista Babatunde Raji Fashola ya ce  rashin zaman lafiya  da kasa ke fama da shi, ba kowa ne ya haddasa  shi ba, illa ’yan kasa su kansu, domin misali, rikicin addini  ba kowa ne ke kawo shi ba, illa mutanen kasar saboda an kasa samun hadin kai da fahintar addinin juna tare […]

Rashin fahimtar juna ke kawo rudani a cikin al’umma – Gwamna Fashola
Rashin fahimtar juna ke kawo rudani a cikin al’umma – Gwamna Fashola

Gwamnan Jihar Legas, Mista Babatunde Raji Fashola ya ce  rashin zaman lafiya  da kasa ke fama da shi, ba kowa ne ya haddasa  shi ba, illa ’yan kasa su kansu, domin misali, rikicin addini  ba kowa ne ke kawo shi ba, illa mutanen kasar saboda an kasa samun hadin kai da fahintar addinin juna tare da mutunta shi, lamarin da zai kawar da duk wani rudani a cikin al’umma.
Gwamnan yana magana  ne sa’ilin da yake karbar bakuncin shugaban cocin Methodist  na kasa a  birnin Ikko,  Dokta Chukwuemeka Uche, inda ya kara da cewa, “Muddin ba za mu dubi kanmu  a matsayin ’yan Najeriya ba, wadanda Allah Ya yi mu iri daban-daban kuma a kasa daya ba, to ba shakka  har kullum za mu ci gaba da samun matsalalar zamantakewa”.
Gwamna Fashola ya ce nauyin samar da kasa dunkulalliya ya rataya a wuyan shugabanni na kowane jinsin jama’a ko addini, saboda haka ya zama wajibi kowa ya yi bakin kokarinsa wajen ganin an mutanta matsayin kasar ba muzanta ta ba. “Matukar kowa ya sauke nauyin da ke kansa, Najeriya za ta bunkasa. Shugabannin addini  na da babban kalubale a gabansu wajen samar da kasa  daya dunkulalliya, domin kuwa batunsu tamkar wahayi yake ga mabiyansu, saboda haka akwai bukatar su fahimtar da mabiyan nasu muhimacin mutunta addinin juna da sanin kimar dan Adam.
Gwamnan ya ce da farko shi gidan mabiya addinin kirista ya tashi, har ya kai dan shekara 20 cocin Methodist yake  zuwa tare da mahaifiyarsa mai bin addinin kirista, kodayake bayan nan ne ya koma bin addinin mahaifinsa na Musulunci, ga shi kuma matarsa mai bin addinin kirista ce. “Mu a nan Legas, an dan jima da fahintar juna a fannin addin, shi ya sa ba a rikicin addini”. Inji shi.
Shi ko Dokta Chukwuemeka cewa ya yi wanda  ya karbi shugabancin cocin daga hannunsa ya  yaba da  irin rawar  da gwamnan ke takawa wajen  taimakon cocin, saboda haka ya yi fata  shi ma zai samu  irin wannan taimakon.
Ya ce kusan kowa  na koyi da Gwamnan Fashola saboda irin ayyukansa da kuma  tsarin tafiyar da mulkinsa, musamman wajen nada wadanda ma ba ’yan kabilar Yarabawa ba a matsayin kwamishina da  mai ba shi shawara, irin shugabannin da  Najeriya ke bukata ke nan.