Rikici tsakanin ƙauyukan Osun ya sa an harbi DPO da wasu ’yan sanda 4

Gwamnan jihar ya kuma ba da umarnin harbi ga duk wanda ya sake tayar da zaune tsaye a yankin

Rikici tsakanin ƙauyukan Osun ya sa an harbi DPO da wasu ’yan sanda 4

Wani sabon rikici a kan jayayyar filaye ya sake barkewa a tsakanin al’ummomin garuruwan Ilobu da Ifon da ke makwabtaka da juna a Jihar Osun.

An fara rikicin ne cikin daren Laraba zuwa wayewar garin Alhamis.

Wata majiya ta ce mutum daya ya rasa ransa a wajen rikicin sannan an yi kone-konen gidaje da kadarori kafin gamayyar jami’an tsaro su shawo kan lamarin.

Wasu majiyoyi a yankin sun shaida wa Aminiya cewa an ga dimbin mutane maza da mata suna kokarin kauracewa garuruwan.

Da take tabbatar da aukuwar lamarin a ranar Laraba, Kakakin Rundunar ’Yan Sanda a Jihar, Yemisi Opalola ta ce an yi wa jami’an ’yan sandan da aka tura su kwantar da rikicin kwanton bauna da aka harbi babban jami’i (DPO) da jami’ansa 4 tare da kona sabuwar motar sintiri a lokacin rikicin.

Kakakin ’yan sandan ta ce duk da yake an shawo kan lamarin sai dai har zuwa lokacin rubuta wannan labari wadannan jami’an ’yan sanda suna kwance a asibiti da likitoci suke kokarin ceton rayukansu.

A wani labarin kuma, Gwamnan Jihar, Ademola Adeleke, ya ba jami’an tsaro umarnin harbin duk wanda aka gani yana kokarin sake tayar da rikici a yankunan.

Gwamnan ya kuma tunatar da mazauna yankin cewa dokar hana fitar da ya sanya har yanzu tana nan daram.

Ukraine ta cimma yarjejeniya da Amurka kan haƙar ma’adinai

Dangote ya rage farashin man fetur zuwa N860 a Legas

Na gaji bashin 8.9bn a matsayin shugaban APC — Ganduje

Boko Haram sun sace mutum 2 da kayan abinci a Borno

Tags