Rundunar ’yan sanda ta gindaya wa masu shirya zanga-zanga sharuɗa

Rundunar ’yan sanda ta ce an ɗauko sojojin haya daga ƙasashen ƙetare a shirye-shiryen shiga zanga-zanga.

Rundunar ’yan sanda ta gindaya wa masu shirya zanga-zanga sharuɗa

Rundunar ’yan sandan Nijeriya ta buƙaci masu shirya zanga-zangar matsin rayuwa a faɗin ƙasar da su miƙa mata bayanansu.

Babban Sufeton ’yan sandan Nijeriya Kayode Egbetokun ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai ranar Juma’a a Abuja.

Kayode Egbetokun wanda ya tabbatar da cewa ’yan kasa na da cikakken ’yancin gudanar da zanga-zanga ta lumana, ya kuma shawarci masu shirya ta da su sake tunani gabanin farawa.

Egbetokun ya ce duk masu shirya zanga-zangar ko ɗaukar nauyi su miƙa wa kwamishinonin ’yan sandan jihohinsu sunayensu da adireshi domin hakan zai tabbatar da cewa an yi zanga-zangar cikin lumana.

Sauran sharuɗan da babban jami’in ’yan sandan ya gindaya sun haɗa da miƙa wa rundunar bayanan hanyoyin da za a bi yayin gudanar da zanga-zangar da kuma wurin haɗuwa da kuma tsawon lokacin da zanga-zangar za ta ɗauka.

Kazalika, Babban Sufeton ’yan sandan ya ce rahotannin sirri sun tabbatar musu an ɗauko sojojin haya daga ƙasashen ƙetare a shirye-shiryen shiga zanga-zangar.

Sai dai shugaban ’yan sandan bai yi wani ƙarin bayani kan zargin shigowar sojojin hayar ƙasashen ƙetare ba cikin zanga-zangar.

“Muna bibiyar yadda lamura ke faruwa kan zanga-zangar da take mana barazana, yayin da wasu ƙungiyoyi ke neman a yi zanga-zangar tashin hankali irin ta Kenya, wasu kuma na kira a kwantar da hankali a yi ta cikin nutsuwa ba tashin hankali.

“Wasu na kiran a yi zanga-zangar nutsuwa amma da kausasan kalamai, wani abu da yake sa mu nazari kan gaskiyar lamarinsu.

“Muna da tarihin zanga-zangar da aka yi ta rikici a Najeriya. A ganina ya kamata mu kalli wasu zanga-zangar da ake yi a wasu ƙasashen da suka zama masu haɗari.

“Muna kira ga ’yan Najeriya masu kishin ƙasa da su janye daga wannan zanga-zanga, saboda illar da ke cikinta da ta fito ƙarara da kuma rashin sani ga matasan da suke kira a yi tashin hankali,” in ji Egbetokun.

Aminiya ta ruwaito cewa, an shirya zanga-zanga a faɗin ƙasar daga 1 ga watan Agusta zuwa 10 saboda tsadar rayuwa.