Ruwa ya ci ’yan mata hudu a Jigawa

Sun nutse a kogi a lokacin da suke kokarin ketarawa su tafi gona a yankin Gwaram, Jihar Jigawa

Ruwa ya ci ’yan mata hudu a Jigawa

’Yan sanda a jihar Jigawa sun tsamo gawarwakin wasu ’yan mata hudu da suka nitse a ruwa a Karamar Hukumar Gwaram ta Jihar.

Rahotanni sun nuna cewa ’yan matan sun nitse a kogin ne lokacin da suke kokarin tsallaka shi domin zuwa gona.

A ranar Talata Kakakin Rundunar ’Yan Sanda a jihar, ASP Abdu Jinjiri shine ya tabbatar da aukuwar lamarin wanda ya ce ya faru ne da misalin karfe 10 na safiyar ranar a kauyen Sara na karamar hukumar ta Gwaram.

Ya ce wadanda iftila’in ya rutsa da su sun hada da Bilkisu Haruna mai kimanin shekara 17; Shamsiyya Nuhu mai shekara 13; da Maryam Danlami mai shekaru 12; dukkansu daga kauyen Kafin Doka Yamma.

Sai dai ya ce har yanzu ana ci gaba da neman gawar wata yarinyar mai suna Marakisiyya Musa mai shekara 12 wacce ba a kai ga gano ta ba.

Mahaifinmu ba shi da ciwon suga – Ɗan Janar Rabe

Sojoji sun daƙile harin Boko Haram, sun ceto mutum 9 a Borno

’Yan sanda sun kashe ’yan fashi 3 a Binuwai

Mahara sun sace bsarake, sun harbi matarsa a ƙauyen Ondo