Sabon harin bom ya jikkata mutum 9 a Taraba
Kwana uku bayan makamancinsa da kungiyar ISWAP ta kashe mutum 30 a wata mashaya
Gwamnan Taraba, Darius Dickson Ishaku
Wani harin bom da aka kai da dare ya yi sanadiyyar jikkata akalla mutum tara Jihar Taraba.
Bom din ya tashi ne ranar Juma’a da dare a unguwar Nukkai da ke kan iyakar Karamar Hukumar Ardo-Kola ta Jihar Taraba.
- Mayakan ISWAP 70 sun mika wuya a Borno
- Ranar littafi ta duniya: ‘Har a nade kasa ba za a daina karanta littafi ba’
Kakakin ’yan sanda na Jihar Taraba, DSP Abdullahi Usman, ya tabbatar wa wakilinmu cewa mutum tara sun samu rauni a harin bom din.
Zuwa lokacin hada wannan rahoto babu cikakken bayani, amma Aminiya ta gano an kai harin ne a kusa da wani gidan giya, kuma ya farfasa jikin gini.
Harim na zuwa ne kwana uku bayan wani makamancinsa da kungiyar ISWAP ta kai wata mashaya a jihar ya kashe mutum 30.
Daga baya kungiyar ISWAP ta yi ikirarin cewa kafirai ne hadafinta a harin da mayakanta suka kai mashayar.