Safarar Mutane: Damuwar Duniya Kan Yadda Najeriya Ta Ciri Tuta
Hukumar Kula da Masu Kaura ta Dunuya ta ja kunnen Najeriya da ta dauki matakin gaggawa don kawo karshen safarar mutane.
Ofishin Hukumar NAPTIP mai yaki da safarar mutane a Najeriya
Albarkacin Ranar Yaki da Safarar Mutane ta Duniya, wadda ke fadowa ranar 30 ga watan Yuli, an ja kunnen hukumomin Najeriya da su dauki matakin gaggawa don kawo karshen lamarin.
Hukumar Kula da Kaurar Jama’a ta Duniya, wadda ta yi kiran, ta ce Najeriya ce kasar da ta fi yawan mutanen da ake safarar su a duniya.