Sajoji sun kaddamar da juyin mulki a Gabon

Sojojin kasar Gabon sun hambarar da gwamnatin mulkin Shugaba Ali Bongo. Rahotanni na bayyana cewa, iyalan gidansa sun shafe shekara 50 suna mulkin kasar mai arzikin man fetur. Sojojin kasar da ke yankin yammacin gabar tekun Afirka ta tsakiya sun ce sun kaddamar da juyin mulki ne “domin dawo da demokradiyya”. Su karbe iko a […]

Sajoji sun kaddamar da juyin mulki a Gabon

Sojojin kasar Gabon sun hambarar da gwamnatin mulkin Shugaba Ali Bongo.

Rahotanni na bayyana cewa, iyalan gidansa sun shafe shekara 50 suna mulkin kasar mai arzikin man fetur.

Sojojin kasar da ke yankin yammacin gabar tekun Afirka ta tsakiya sun ce sun kaddamar da juyin mulki ne “domin dawo da demokradiyya”.

Su karbe iko a babbar tashar talabijin ta kasar da karfe 4 na asuba agogon kasar (Karfe 3 GMT), kuma sun karanta wata gajeriyar sanarwa da ta bayyana cewa sun kafa “Majalisar Ceton Kasa”.

Shugaba Ali Bongo ya dare bisa karagar mulki a 2009 kuma ya shafe fiye da wata biyu yana jinya a wajen kasar.

Kamar yadda rahoton BBC ya sanar.

Sojoji sun kashe kwamandan ’yan bindiga da tarwatsa 300

Zaɓen 2027: Tinubu ya sake tsayar da Shettima mataimakinsa

Tinubu ya gaji yana buƙatar ya huta — Peter Obi

Ɗalibai da malamai da aka sace a Oyo sun kuɓuta