Sakkwato za ta kashe Naira miliyan 174 don ciyarwar azumi

Gwamnatin Jihar Sakkwato za ta kashe Naira miliyan 174 kan ciyar da al’umma a lokacin azumin watan Ramadan na bana, a cibiyoyi 84 da ke cikin birnin Sakkwao da wajensa.Gwamnan Jihar, Alhaji Aliyu Magatakarda Wamakko ne ya sanar da haka a wurin bikin gidauniyar Naira miliyan 25 da kungiyar Izala ta shirya a matakin jiha […]

Sakkwato za ta kashe Naira miliyan 174 don ciyarwar azumi
Sakkwato za ta kashe Naira miliyan 174 don ciyarwar azumi

Gwamnatin Jihar Sakkwato za ta kashe Naira miliyan 174 kan ciyar da al’umma a lokacin azumin watan Ramadan na bana, a cibiyoyi 84 da ke cikin birnin Sakkwao da wajensa.
Gwamnan Jihar, Alhaji Aliyu Magatakarda Wamakko ne ya sanar da haka a wurin bikin gidauniyar Naira miliyan 25 da kungiyar Izala ta shirya a matakin jiha a Masallacin Rokon Ruwa da ke Unguwar Gayu a birnin Sakkwato.
Gwamnan wanda Kwamishinan Al’amuran Addinin Musulunci, Alhaji Tukur Alkali ya wakilta ya ce sun yi shiri gamsasshe domin taimaka wa al’ummar jihar a lokacin azumi da kuma sauran lokutan da ba na azumi ba, saboda a kowace shekara sukan kara kudi ne domin la’akari da bukatun al’umma musamman masu azumi.
A cewarsa, an kirkiro ma’aikatar ce domin taimaka wa jama’a ta fannin addini kuma sun gina makarantun Islamiyya da yawa a jihar da ba ladanai da limamai albashi a kowane wata da gyara gidajensu.