Sallah: Gwamnatin Najeriya ta ayyana hutun kwana biyu

Za a yi hutun ne ranakun Litinin da Talata

Sallah: Gwamnatin Najeriya ta ayyana hutun kwana biyu

Ministan Harkokin Cikin Gida, Rauf Aregbesola

Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata, 11 da 12 ga watan Yuli a matsayin ranakun hutu domin bukukuwan Sallar Layya a Najeriya.

Ministan Hrkokin Cikin Gida, Rauf Aregbesola ne ya bayyana haka, a cikin wata sanarwa da ya fitar a madadin Gwamnatin Tarayya, dauke da sa hannun Babban Sakataren ma’aikatar, Shuaib Belgore a ranar Alhamis.

Ya kuma taya dukkan Musulman Najeriya na gida da na ketare murnar zagayowar lokacin.

Aregbesola ya ce, “Ina kira ga Musulmai da su ci gaba da yada halayen kaunar juna, zaman lafiya, tausayi da sadaukarwa, kamar yadda Annabi Muhammad (S.A.W) ya koyar.

“Ina kuma rokon su da su yi amfani da lokacin wajen yi wa Najeriya addu’ar samun zaman lafiya, hadin kai da ci gaba, la’akari da halin da ake ciki a yanzu.”

Ministan ya kuma ba da tabbacin cewa gwamnatin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ta damu matuka kuma tana iya bakin kokarinta wajen kare rayuka da dukiyoyin ’yan Najeriya da kuma inganta rayuwarsu.