Sanatan Amurka ya sake zargin Najeriya kan muzguna wa Kiristoci
A cikin saƙon da ya wallafa a shafinsa na X, Cruz ya yi iƙirarin cewa, wasu manufofi da hukumomin Najeriya ke aiwatarwa sun taimaka wajen haifar da hare-hare kan Kiristoci
Sanatan Amurka Ted Cruz ya zargi gwamnatin Najeriya da mayar da hankali kan fafutikar na kare martabarta a ƙasashen waje, maimakon magance zarge-zargen da ake yi na muzguna wa Kiristoci da sauran tsirarun masu addini.
A cikin saƙon da ya wallafa a shafinsa na X, Cruz ya yi iƙirarin cewa, wasu manufofi da hukumomin Najeriya ke aiwatarwa sun taimaka wajen haifar da hare-hare kan Kiristoci da sauran tsiraru.
- 2027: A guji tikitin Gwamna masu addini ɗaya — Sheikh Maraya
- ’Yan bindiga sun kai hari da kashe manoma 23
Ya ce, yana ci gaba da neman a qaqaba wa wasu jami’an Najeriya takunkumi saboda abin da ya kira take ’yancin addini.
Sai dai gwamnatin Najeriya ta sha musanta waɗannan zarge-zarge, tana mai cewa, ba ta da hannu a muzgunawa mabiyan wani addini.
A baya gwamnatin ta ɗauki Kamfanin hulɗa da jama’a na Amurka domin bayyana matakan da take ɗauka wajen yaƙi da ta’addanci da kuma kare al’ummomin Kirista.
Rahotanni sun kuma nuna cewa, gwamnatin tarayya ta ware kuɗaɗe domin yaƙi da abin da ta kira yaɗa farfagandar da ke zargin Najeriya da muzgunawa Kiristoci.