Sarkin Musulmi ya sanar da ganin watan Babbar Sallah a Najeriya

Hakan na nufin Alhamis ce daya ga wata

Sarkin Musulmi ya sanar da ganin watan Babbar Sallah a Najeriya

Mai alfarma Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar

Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III ya tabbatar da ganin jinjirin watan Zul-Hijjah a Najeriya, wanda hakan ya tabbatar da ranar Alhamis a matsayin ranar daya ga watan.

Sarkin, wanda kuma shi ne Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci a Najeriya (NSCIA) ya ce ranar dai ita ce ta yi daidai da 30 ga watan Yunin 2022.

Hakan dai na nufin a bana za a yi bikin Sallah Babba ranar Asabar, tara ga watan Yulin 2022.

Watan Zul-Hijjah dai shi ne watan na 12 kuma na karshe a kalandar Musulunci, kuma a cikinshi ne Musulmai daga ko ina daga fadin duniya ke gudanar da Aikin Hajji a kasar Saudiyya.

Kazalika, yayin bikin Sallar, Musulmai kuma na gudanar da ibadar Layya, inda sukan yanka dabbobi domin raba naman ga ’yan uwa da mabukata.

Zazzaɓin Lassa ya kashe mutum 214 a Najeriya — NCDC

An kama masu garkuwa da mutane a Borno 

Rikicin ya kunno kai a Hukumar Alhazan Jihar Delta

Sojoji sun ceto mutane 5 da ISWAP ta sace a Harin Ngoshe